in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dattawan Najeriya tana fatan kawo karshen shigo da man-ja cikin kasar
2018-02-14 09:05:17 cri

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya Ike Ekweremadu ya bayyana cewa, majalisar dattawan kasar ta kada kuri'ar da za ta kawo karshen hana shigo da man-ja da ma dangin kayayyakin da ake samarwa daga gare shi cikin kasar.

Ekweremadu wanda ya bayyana hakan a jiya Talata, ya ce majalisar ta dauki wannan mataki ne don ceto sashen da ma manoma cikin gida, da kuma yadda za a bunkasa da kiyaye yadda ake samar da man-ja a cikin kasar.

Bugu da kari, wannan mataki zai taimakawa wajen farfado da bangaren samar da man-jan, ya kuma sanya shi bisa turbar da ta dace ta yadda zai taka rawar da ta dace a matsayin daya daga sassan dake samarwa kasar kudaden shiga, baya da samar da guraben ayyukan yi ga 'yan kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China