in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yong ya gana da shugaban hukumar zartaswar kungiyar AU
2018-02-09 20:10:48 cri
A yau Jumma'a ne, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin Wang Yong ya gana da shugaban hukumar zartarwas kungiyar AU Moussa Faki.

A yayin ganawar, Wang Yong ya bayyana cewa, Sin tana dora muhimmanci sosai kan dangantakar dake tsakaninta da kasashen Afirka, kana tana son kara raya dangantakar abokantaka a tsakaninta da kungiyar AU, da kara yin mu'amala kan manyan manufofin samun bunkasuwa, da sa kaimi ga raya hadin gwiwarsu da samun ci gaba tare.

A nasa bangare, Faki ya nuna godiya ga kasar Sin bisa ga goyon baya da take nunawa ga sha'anin samun bunkasuwar nahiyar cikin lumana da kuma raya kungiyar AU. Kana kungiyar AU tana son hada kai tare da kasar Sin wajen ganin an samu nasarar shirya taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da za a yi a birnin Beijing a bana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China