in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da AU sun tabbatar da fannoni 5 da za su yi hadin gwiwa
2018-02-08 19:38:39 cri

A yau Alhamis ne Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin, da Moussa Faki, shugaban hukumar zartaswar kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU, wanda ke ziyara a kasar Sin, suka jagoranci babban taron musayar ra'ayi kan manyan tsare-tsare karo na 7 tsakanin Sin da kungiyar AU, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A yayin taron, jami'an 2 sun tattauna yadda za su zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, sa'an nan sun tabbatar da fannoni 5 da za su yi kokarin gudanar da hadin gwiwa. A cewar mista Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin, wadannan fannoni 5 sun hada da, kara karfin kungiyar AU na daidaita al'amura, da kara gina kayayyakin more rayuwa a nahiyar Afirka, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afirka, da raya harkokin kula da lafiyar jikin jama'a da jinyar wadanda suka kamuwa da cututtuka a Afirka, gami da karfafa hadin gwiwa a fannin yawon shakatawa da zirga-zirgar jiragen sama.

A cewar jami'in kasar Sin, hadin gwiwa a wadannan fannoni sun shafi daukacin nahiyar Afirka, zai kuma kyautata huldar dake tsakanin kasar Sin da kungiyar ta AU.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China