in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin musamman MDD ta yi gargadi game da cigaba da shigar da makamai cikin Libya
2018-02-08 10:47:44 cri
Shugaban shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a Libya Ghassan Salame, ya tabbatar da cewa makamai na cigaba da bazuwa a cikin kasar Libya sakamakon rashin cikakken tsarin hukumomin dake kula da kan iyakokin kasar.

Salame, wanda kuma shi ne wakilin musamman na sakatare janar na MDD, ya bayyana hakan ne bayan wani taron ganawa da wakilan siyasa da masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro na kudancin Libya inda suka tattauna game da batun matsalolio dake addabar biranensu, musamman matsalar tabarbarewar tsaro a kan iyakokinsu.

Salame ya fadawa taron 'yan jaridu a Tripoli cewa, dole ne a magance matsalar yaduwar makamai ba bisa ka'ida ba a kasar, ya kara da cewa ba'a sanya ido a kan iyakokin kasar kuma babu wani tsarin bai daya na hukumomin kasar Libya dake hana bazuwar makamai.

A cewarsa MDD tana aiki tukuru kuma tana tuntubar kasashen duniya masu yawa don hana shigar da makamai cikin kasar ta Libya.

Sai dai wannan jami'in MDDr bai ayyana kasashen da yake tattaunawa da su wajen hana shigar da makamai cikin kasar Libyan ba. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China