in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNFPA ya bukaci a hanzarta kawo karshen kaciyar mata a duniya
2018-02-08 09:13:15 cri
A yayin da kasar Ghana ta bi sahun takwarorinta na duniya wajen gudanar da bikin tunawa da ranar yaki da kaciyar mata ta duniya, asusun kula da yawan al'umma na MDD (UNFPA) ya bukaci a hanzarta daukar matakan kawar da dabi'ar kaciyar mata a duniya baki daya.

Niyi Ojuolape, wakilin UNFPA a Ghana, ya bayyana cewa, illolin dake tattare da wannan dabi'a yana hana mata da 'yan mata yancin jin dadin rayuwarsu da kuma hana su samun damammakin da suka dace, inda ya bukaci masu kishin al'umma a kasar Ghana da su tsaya tsayin daka don yakar wannan muguwar dabi'a.

Shi dai kaciyar mata ana yanke wani sashe ne daga al'aurar mace a matsayin al'ada ko kuma wasu dalilai da ba su shafi na kiwon lafiya ba.

Ghana tana daga cikin kasashe 29 na Afrika da yankin gabas ta tsakiya, inda ake fama da wannan al'ada, duk kuwa da kokarin da ake yi na neman kawo karshen dabi'ar kaciyar matan.

Ojuolape, wanda kungiyarsa ke fafutukar yaki da dabi'ar kaciyar mata, ya bayyana cewa, binciken kimiyya ya gano cewa wannan dabi'a tana da matukar illa kuma bai dace a cigaba da gudanar da ita a wannan zamani ba. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China