in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan wadanda cutar Lassa ta hallaka a Najeriya ya kai mutane 30
2018-02-05 09:27:53 cri

Gwamnan jihar Ondo dake kudancin Najeriya Oluwarotimi Akeredolu, ya ce sakamakon bincike a dakunan gwaji, ya tabbatar da kamuwar mutane 36 da zazzabin Lassa a jihar ta Ondo, ciki hadda mutane 9 da tuni suka riga mu gidan gaskiya.

Gwamna Akeredolu ya ce, gwamnatin sa ta kaddamar da shirin gaggawa na yaki da yaduwar cutar a mataki na jiha da na kananan hukumomi.

Cutar zazzabin Lassa dai ta barke ne a farkon watan Janairun da ya gabata kamar yadda mahukuntan kasar suka tabbatar.

A makon jiya, babban darakta mai kula da cibiyar yaki da cututtuka ta Najeriya Chikwe Ihekweazu, ya shaidawa taron manema labarai cewa, zazzabin na Lassa ya hallaka mutane 21 a Najeriya.

Cutar zazzabin Lassa dai wasu nau'in kwayoyin cuta ne dake iya yaduwa a kowane lokaci ko yanayi ke haifar da ita, ko da yake ta fi kamari a lokacin bazara. Ana kuma iya kandagarkin yaduwar ta ta hanyar kula da tsaftar muhalli, da kaucewa taba duk wani abu da bera ya taba, tare da tsaftace gida yadda ya kamata.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China