A ranar Talata Najeriya ta bayyana cewa, an samu bullar cutar zazzabin Lassa a jihar Plateau, sai dai kuma ana ci gaba da hada karfi da karfe domin dakile bazuwar cutar a kasar.
Kuden Deyin, shi ne kwamishinan lafiya na jihar Plateau, ya bayyana cewa, an samu bullar zazzabin na Lassa guda hudu ne ta hanyar ta'ammali da halittu dangin beraye.
Daga cikin mutanen 4 da suka kamu da cutar, an tabbatar da mutuwar mutum guda, yayin da ragowar mutanen 3 suke samun kulawa a asibiti.(Ahmad Fagam)