in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar 'yan tawayen Sudan ta kara wa'adin tsagaida bude wuta a kudancin Kordofan da Blue Nile
2018-01-31 09:58:26 cri
Kungiyar 'yan tawayen Sudan bangaren arewaci ta sanar da tsawaita wa'adin tsagaida bude wuta a yankunan kudancin Kordofan da Blue Nile har zuwa watanni hudu tun daga ranar 1 ga watan Fabrairun wannan shekara.

Shugaban 'yan tawayen bangaren arewaci Abdel Azizi al-Hilu wanda ya sanar da hakan a jiya Talata, ya ce wannan mataki wata dama ce ta kawo karshen rikicin Sudan cikin ruwan sanyi. A don haka ya umarci dukkan rundunonin soja dake karkashin kungiyar, da su martaba wannan kuduri.

Mahukuntan Sudan da kungiyar dai sun sha tsawaita wa'adin tsagaita bude wuta daga lokaci zuwa lokaci a yankunan kudancin Kordofan da Bule Nile.

A ranar 3 ga watan Fabrairu mai kamawa ne ake saran za a koma teburin tattaunawar zaman lafiya tsakanin sassan biyu dangane da Kudancin Kordofan da Bule Nile a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

Wata tawagar sasantawar kungiyar tarayyar Afirka(AU) karkashin jagoarcnin tsohon shugaban Afirka ta kudu Thabo Mbeki ne suke sa-ido a tattaunawa tsakanin sassan biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China