in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: An kashe ma'aikatan agaji 95 a Sudan ta kudu cikin shekaru hudu
2018-01-19 12:15:04 cri
Hukumar kula da harkokin jin kai ta MDD(OCHA) ta bayyana cewa, kimanin ma'aitakan agaji 95 ne suka gamu da ajalinsu a Sudan ta kudu tun lokacin da rikici ya barke a kasar a watan Disamban shekarar 2013.

Ofishin hukumar ta OCHA ya bayyana cewa, a shekarar 2017 da ta gabata, an samu karuwar rahotanni kisan ma'aikatan agaji mafi yawa, inda aka kashe ma'aikatan agaji 28. MDD dai ta ce irin wadannan kashe-kashe sun hada da na ma'aikatan agaji, ko fashi da makami, kwashe kayayyakin agaji da barazana ko tursasawa, kuma galibi sun faru ne a yankunan Juba, Rubkona da Wau. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China