Amurka: Rasha ta yarda a jibge karin sojojin wanzar da zaman lafiya a Ukraine
Kurt Volker, manzon musamman na gwamnatin kasar Amurka mai kula batun Ukraine, ya furta a jiya Litinin cewa, gwamnatin kasar Rasha ta sasauta ra'ayinta game da jibge sojojin wanzar da zaman lafiya na MDD a yankin Donbas dake fama da tashin hakali na kasar Ukraine, inda kasar ta yarda a fadada aikin wanzar da zaman lafiya zuwa daukacin yankin da ake fama da tashin hakali.(Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku