in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya halarci taron ministocin dandalin China-CELAC
2018-01-23 11:17:43 cri
A ranar 22 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci taron ministocin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Latin Amurka da yankin Caribbean wato China-CELAC karo na biyu da aka gudanar a birnin Santiago na kasar Chile.

A gun taron, an zartas da sanarwar Santiago, da shirin ayyukan hadin gwiwar Sin da kasashen Latin Amurka da yankin Caribbean kan manyan fannoni tun daga shekarar 2019 zuwa 2021. Kana an zartas da sanarwar musamman kan shawarar "ziri daya da hanya daya". Bayan taron, Wang Yi da ministan harkokin wajen kasar Chile da na Salvador sun gana da 'yan jarida tare.

A gun taron, daya bayan daya Wang Yi ya gana da ministan harkokin wajen kasashen Chile, Cuba, Peru, Mexico, Venezuela, da sauran kasashen dandalin tattaunawar, kana sun gana da ministocin harkokin wajen kasashen yankin Caribbean 9 wadanda suka kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu da kasar Sin, tare da shugabannin kungiyoyin yankin Latin Amurka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China