in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: karuwar masana'antu ta zarce kaso 3 na GDPn kasar Sin
2018-01-30 13:41:16 cri
Miao Xu, ministan masana'antu da aikin sadarwa na kasar Sin ya furta a yau a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin cewa, masana'atun kasar sun bunkasa yadda ya kamata a shekarar 2017 da ta gabata, inda ci gaban da aka samu ya wuce yadda aka zata.

Alkaluman kididdigar sun nuna cewa, karuwar kudin da aka samu a fannin masana'antu ta kai kudin Sin RMB Yuan biliyan 28000, wadda ta kai kashi 33.9% na kudin kayayyakin da ake fitarwa a kasar wato GDP, jimillar da ta karu da kashi 0.54% bisa dari a shekarar ta bara.

Ban da haka kuma, kudin shiga da kamfanonin kasar Sin suka samu ya fi yawa a shekarar ta 2017, idan an kwatanta da na shekarun da suka gabata, kama daga shekarar 2013.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China