in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: Sabuwar tashar jiragen ruwa ta Lekki za ta samar da alfanu sosai
2018-01-30 13:26:45 cri
Jaridar Daily Trust da ake wallafawa a kasar Najeriya ta fitar da wani labari a jiya Litinin dake cewa, babban darektan hukumar gina kayayyakin more rayuwa ta ICRC, Chidi Izuwah, ya bayyana cewa, bayan da aka kammala gina babbar tashar jiragen ruwa a yankin Lekki dake jihar Lagos, mataki zai baiwa gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi daban daban na kasar amfana da kudaden da yawansu zai kai kimanin dalar Amurka biliyan 361.

Jami'in ya yi wannan furuci ne bayan wani rangadin da ya kammala a tsibirin Lekki a Jumma'ar da ta gabata, inda ya kara da cewa, hukumomin kasar za su samu kudin da ya kai kimanin dalar Amurka biliyan 201 daga harajin da za a tara kan ayyukan da za a gudanar a tashar jiragen ruwan. Ban da haka, tashar jiragen ruwa za ta baiwa yankin ciniki cikin 'yanci na Lekki damar samun karin guraben ayyukan yi fiye da dubu 170, inda yawan kudin albashin da ma'aikatan tashar za su samu zai kai kimanin dalar Amurka biliyan 20.

Bisa shirin da aka yi, tashar jiragen ruwa ta Lekki za ta kasance a tsakiyar yankin ciniki cikin 'yanci na Lagos, kuma za ta taimaka wajen raya tattalin arzikin kasar Najeriya da tallafawa harkokin cinikayya a daukacin yankin yammacin Afirka, gami da zama wata babbar cibiyar jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa ta kasa da kasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China