in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun cafke mutanen da suke zargi wajen batan sojoji a arewa maso gabashin kasar
2018-01-26 10:24:28 cri
Rundunar sojin Najeriya ta ce ta kama mutane 11 da take zarginsu da hannu wajen salwantar wani daga cikin dakarunta a kauyen Opallo a jihar Adamawa dake arewa maso gabashin kasar.

Birgediya janar Bello Mohammed, shi ne kwamandan runduna ta 23 ta sojojin kasar ya tabbatar da hakan ga 'yan jaridu a Yola, babban birnin jihar ta Adamawa, ya ce daga cikin wadanda aka damke har da wani hakimi.

Mohammed ya ce, dakarun sojin kasar suna cigaba da gudanar da bincike don gano sojan da ya bace.

A wani labarin kuma, mazauna kauyen na Opallo sun fara tsarewa saboda fargaba, inda wasu ke zargin cewa sojoji sun cinna wuta a wasu sassa na kauyen.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China