in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rwanda ta lallasa Equatorial Guinea da ci 1-0 a wasan cin kofin kasashen Afrika
2018-01-25 14:56:12 cri
Rwanda ta doke Equatorial Guinea da ci 1 da nema a wasan kofin kwararru na kasashen Afrika wato (CHAN), matakin da ya bata kwarin gwiwa zuwa matsayi na kusa da na kusan karshe a gasar.

A wasan da aka buga a katafaren filin wasa na Grand Stade na birnin Tangier na kasar Morocco a ranar Juma'a, dan wasa Thierry Manzi ya kasance a matsayin gwarzon dan wasa a wasan, wanda ya samu nasarar zara kwallo bayan mintoci 67 da fara wasan, dan wasan ya kware matuka wajen buga kwallo da ka, lamarin da ya bashi damar samarwa Rwandan maki uku nan take.

Nasarar dai ta daga matsayin kasar Rwanda zuwa rukuni guda da Najeriya wato rukunin C da maki 4, sai kuma Libya wanda ke bi musu baya da maki 3.

A halin da ake ciki, kungiyoyin wasanni 3 ne zasu kara a wasan kusa dana karshe, a rukunin C.

A ranar Talata, Rwanda zata kara da Libya yayin da Najeriya zata taka leda da Equatorial Guinea.

A rukunin A Morocco da Sudan zasu kara, sai kuma Zambia da Namibia zasu kara a rukunin B, kuma tuni an riga an kammala tsara samar musu da gurabe a wasan kusa dana kusan karshe cikin wannan mako bayan sun samu nasarar lashe wasanninsu biyu na farko.

Wasannin dai na kwallon kafan 'yan kasashen Afrika ne na sada zumunta, wadanda ya kunshi kungiyoyin wasa 16 a rukunoni 4.

Daga kowane rukuni, kungiyoyi biyu dake kan gaba ne zasu halarci wasan kusa na kusan karshe.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China