in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na da karfin gwiwar samun gurbin buga gasar matasa 'yan kasa da shekaru 20
2018-01-10 16:05:35 cri
Mahukuntan kungiyar kwallon kafar mata ta Najeriya matasa 'yan kasa da shekaru 20 wadda ake wa lakabi da Falconets, ta bayyana kyakkyawan fata na samun gurbin buga gasar cin kofin duniya da zai gudana a watan Agustan bana a kasar Faransa.

A ranar Laraba ne dai kungiyar za ta bar gida gabanin wasan ta na neman gurbi da za ta buga da Afirka ta kudu ranar Asabar, kamar dai yadda babban kocin kungiyar Christopher Danjuma ya shaidawa manema labarai a birnin Abuja fadar mulkin Najeriya. Duk kungiyar da ta yi nasara tsakanin kasashen biyu, bayan buga zagaye 2 na wasanni za ta samu daya daga tikiti 2 na buga gasar ta duniya.

Kungiyar ta mata ko Falconets, ta shiga dukkanin gasannin da aka buga ajin na mata 'yan kasa da shekaru 20 tun fara buga gasar a shekarar 2002, wadda a wancan lokacin hukumar FIFA ta sanyawa suna gasar zakarun 'yan kwallo ta mata 'yan kasa da shekaru 19, inda a lokacin duk wacce ta wuce shekaru 19 ba za ta buga gasar ba.

Daga bisani kuma a shekarar 2006 aka kara yawan shekarun zuwa 20. Kana a shekarar 2008 kuma aka mayar da ita gasar cin kofin duniya ta mata.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China