in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco, da Cote d'Ivoire zasu karfafa hadin gwiwa a fagen wasannin
2018-01-25 14:55:15 cri
Kasashen Morocco da Cote d'Ivoire sun rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa a fagen wasannin motsa jiki.

Ministan wasanni da al'amurran matsa na kasar Morocco, Rachid Talbi Alami, da takwaransa na Ivory coast, Francois Albert Amichia, sune suka jagoranci rattaba hannu kan yarjejeniyar ta tsawon shekaru 5, wanda aka kullata da nufin karfafa mu'amala ta fuskar bada horo da kuma kyautata alaka a fagen wasanni tsakanin kasashen biyu.

Kasashen biyu, zasu dinga yin musayar kwarewa da musayar bayanai a sha'anin gudanar da al'amurran wasanni da samar da kayayyakin wasanni, da magungunan da suka shafi wasanni, da kuma yaki da matsalar yin zamba da tada husuma a filayen wasanni.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
ga wasu
v Mene ne wasan kwallon zilliya?  2018-01-21 10:15:06
v Wasan Triathlon da ya kunshi wasanni uku 2017-12-29 06:37:26
v Za a yi bikin nuna wasannin kwamfuta a Zhangzhou 2017-12-20 16:45:39
v Wasan roller skating 2017-12-15 13:47:07
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China