in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bukaci a zurfafa gyare-gyare a kasar
2018-01-24 11:18:59 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci wani taron da aka kira a jiya Talata da nufin tattauna matakan zurfafa gyare-gyare a kasar.

Shugaban ya yi jawabi a wajen taron inda ya bayyana cewa, a shekarar 2018 da muke ciki an fara aiwatar da manufofin da aka gabatar a wajen babban taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 19, kana wannan shekara ita ce cikar shekaru 40 da aka gabatar da manufar gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje a kasar ta Sin, saboda haka ya kasance wani lokaci mai muhimmanci domin gudanar da matakan gyare-gyare a kasar yadda ake bukata. A cewar shugaban, kamata ya yi, a kara kirkiro sabbin fasahohi, da daidaita tunanin mutane, don zurfafa gyare-gyaren da ake yi a kasar.

Ban da haka kuma, mahalarta taron sun jaddada cewa, ya kamata a yi kokarin kawar da wasu matsaloli masu alaka da tsare-tsaren kasar a fannoni daban daban, haka kuma a kara yin kwaskwarima ga wasu fannoni musu muhimmanci da suka hada da kamfanonin mallakar gwamnati, da kare ikon mallakar kadarori, harkokin kudi da haraji, da aikin raya yankunan karkara, da aikin kiyaye muhallin halittu, da dai makamantansu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China