in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya mika wasikar taya murnar bude taron ministocin dandalin China-CELAC
2018-01-23 11:09:17 cri
A ranar 22 ga watan nan ne aka bude taron ministoci karo na biyu na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen Latin Amurka da yankin Caribbean wato China-CELAC a kasar Chile. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika wasika don taya murnar budewar taron.

A cikin wasikar, Xi Jinping ya nuna cewa, bayan da aka gudanar da taron ministocin karo na farko a watan Janairu na shekarar 2015, bisa kokarin bangarorin biyu, China-CELAC ya riga ya zama wata muhimmiyar hanya ta hadin gwiwar Sin da kasashen Latin Amurka da yankin Caribbean, ya kuma sa kaimi ga samun nasarori na hadin gwiwarsu a fannoni daban daban.

Xi Jinping ya jaddada cewa, a tarihi, Sin da kasashen Latin Amurka da yankin Caribbean sun bude hanyar siliki a kan tekun Pasifik. A kuma yanzu, bangarorin biyu na tsara sabon shiri bisa shawarar "ziri daya da hanya daya", a kokarin inganta hadin gwiwarsu da ya ratsa tekun Pasifik, ta yadda za su bude wani sabon babi na raya dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China