in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron AU dake karatowa zai mai da hankali kan yaki da cin hanci
2017-12-27 11:13:38 cri
Tarayyar Afrika ta sanar da cewa taronta na gama gari karo na 30, na shugabannin kasashe da Gwamnatoci, zai gudana daga ranar 22 zuwa 29 ga watan Junairun sabuwar shekara a Addis Ababa babban birnin kasar Habasha.

Bisa Jadawalin taron, za a gudanar da taron gama gari karo na 35 na wakilan kwamitin dindindin daga ranar 22 zuwa 23 ga watan Junairu, sannan a gudanar da karo na 32 na taron majalisar zartarwar Tarayyar daga ranar 25 zuwa 26.

Taken taron da zai gudana a hedkwatar Kungiyar dake Addis Ababa shi ne 'nasarar yaki da cin hanci: hanya mai dorewa ta sauya nahiyar Afrika'.

A cewar Tarayyar, taron gama gari na shugabannin kasashen zai gudana daga ranar 28 zuwa 29 ga watan na Junairu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China