Ana saran kasashe da ba mambobin OPEC ba zasu kara adadin man da suke hakowa a 2018
An samu karuwar adadin hako danyen mai a watan Disamba, kana ana saran adadin zai sake karuwa a shekarar 2018 na adadin hako danyen man daga kasashen da ba mambobin OPEC ba, kamar yadda rahoton kungiyar kasashe masu arzikin man fetur wato OPEC ta fitar.
Rahoton yace hakan ya faru ne sakamakon yadda aka yi hasashen karuwar hako danyen man daga kasashen Amurka Canada, Mexico, Birtaniya, Denmark, Indonesia, Brazil, Latin America da sauransu. (Ahmad)