in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Kar a janyo baraka ga gamayyar kasa da kasa
2018-01-17 20:58:38 cri
A yau Laraba, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya mayar da martani kan shawarar da kasashen Amurka da Canada suka gabatar, dangane da kiran wani taron ministocin waje don tattauna batun nukiliya na kasar Koriya ta Arewa, inda ya bukaci a daina janyo baraka tsakanin gamayyar kasa da kasa.

A wajen taron manema labaru da aka kira yau a birnin Beijing na kasar Sin, wani dan jarida ya yi tambaya cewa, "a ranar Talata, kasashen Canada da Amurka sun yi kira ga wasu kasashen da su ma suka taba tura sojoji don halartar yakin da aka yi a zirin Koriya a shekarar 1950, su gudanar da wani taron ministocin harkokin waje a birnin Vancouver na kasar Canada, inda ake da niyyar matsawa kasar Koriya ta Arewa lamba iya bakin kokarinsu, to, mene ne ra'ayin kasar Sin dangane da batun?"

Game da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya amsa da cewa shawarar da Canada da Amurka suka gabatar ta nuna ra'ayinsu na tsohon yayi irin na yakin cacar baki, wanda zai janyo baraka tsakanin gamayyar kasa da kasa kawai, maimakon taimakawa daidaita batun nukiliyar zirin Koriya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China