in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama mutane a kalla 778 a zanga-zangar da ta barke a wurare da dama a Tunisiya
2018-01-12 19:45:11 cri
A ci gaban zanga-zangar da ta barke a ranar 8 ga wata a kasar Tunisiya, zanga-zangar ta rikide zuwa rikici na nuna karfin tuwo a jiya Alhamis. Ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta ce, rikicin ya haddasa mutuwar mutum guda, tare kuma da jikkatar ma'aikatan tsaro sama da 96, baya ga motocin 'yan sanda sama da 87 da aka lalata. Ya zuwa yanzu, an kama mutane a kalla 778.

An soma zanga-zangar ce a ranar 8 ga wata a birnin Tunis, babban birnin kasar, kuma nan da nan ta bazu zuwa larduna fiye da 10 na kasar. Rahotanni na cewa, zanga-zangar ta barke ne sakamakon matsalar kuncin rayuwa da jama'a ke fuskanta, 'yan kasar na fama da tsadar rayuwa, amma dokar kudi ta shekarar 2018 da gwamnatin kasar ta kaddamar ta sa farashin kaya na ci gaba da karuwa.

Firaministan kasar Tunisiya Youssef Chahed ya bayyana cewa, gwamnati ta fahimci bukatun jama'a, amma ba za ta lamunci tashin hankali da zagon kasa ba, kana duk wanda ya karya doka za a hukunta shi. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China