in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga 2 sun hallaka kana wasu 4 an cafke su a yayin sintirin jami'an tsaron kasar Tunisiya
2017-05-01 12:53:10 cri
Firaministan kasar Tunisiya Youssef Chahed, ya bayyana cewa, a kalla 'yan bindiga biyu aka hallaka, ciki har da dan kunar bakin wake, a lokacin wani simame da jami'an tsaron kasar suka kaddamar a jiya Lahadi a birnin Sidi Bouzid dake tsakiyar birnin Tunisia.

Wata majiyar jami'an tsaron kasar data nemi a sakaye sunanta ta shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, an damke wasu mayakan 4 da ransu.

Wasu kwarrarrun bangarori na jami'an tsaron kasar ne suka kaddamar da simamen, cikinsu har da wata rundunar tsaron kasar ta musamman, wacce ta shafe makonni masu yawa tana farautar mayakan.

Youssef Chahed ya sanar a cibiyar horas da jami'an tsaron kasar dake Bir Bouregba mai tazarar kilomita 60 daga Tunis babban birnin kasar cewa, bayan gudanar da bincike da jami'an tsaron suka yi cikin makonnin da suka wuce, sun yi nasarar gano maboyar 'yan bindigar inda daga bisani suka yi musu dirar mikiya suka hallaka biyu daga cikinsu kana suka kama wasu da ransu.

A cewar Chahed, 'yan kungiyar masu tsattsaunaran ra'ayin addini sun yi yunkurin kaddamar da hare haren ta'addanci a kasar ne a lokacin watan Ramada mai tsarki dake tafe.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China