in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaban Faransa a kasar Sin ta samu cikakkiyar nasara
2018-01-11 19:12:47 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya ce, ziyarar da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya kawo kasar Sin ta samu cikakkiyar nasara.

Lu ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka yi yau Alhamis a nan birnin Beijing, inda ya kara da cewa, kasashen Sin da Faransa sun samu sakamako mai kyau a fannonin siyasa, tattalin arziki da cinikayya, al'adu da dai sauransu. Wannan ya nuna kyakkyawar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, ta kuma aza harsashi mai kyau wajen bunkasa dangantakar dake tsakaninsu a sabon zamani.

Kwanan baya ne, shugaba Emmanuel Macron na kasar Fransa ya kammala ziyarar da ya ke a nan kasar Sin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China