in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tashin hankali ya hallaka mutane 433 a Libya cikin shekarar 2017
2018-01-02 11:10:34 cri
Wani rahoton da hukumar kare hakkin dan adam ta kasar Libya ta fitar a ranar Litinin ya nuna cewa, tashin hankalin da ya barke a kasar yayi sanadiyyar mutuwar mutane kimanin 433 a Libyan cikin shekarar 2017.

Rahoton yace, daga cikin adadin mutanen 433 da suka mutu har da kanana yara 79 da kuma mata 10.

Baki daya an hallaka mutane kimanin 201 a kisan kiyashin da suka faru a sassan kasar daban daban, musamman wadanda kungiyoyin masu dauke da makamai suka kaddamar.

Bugu da kari, an hallaka fararen hula kimanin 157 a sanadiyyar nakiyoyi da aka binne a karkashin kasa a yankunan Benghazi, Sirte da Derna, inji rahoton.

Hukumar ta tabbatar da cewa an kama mutane 143 inda aka muzguna musu, yayin da aka yi garkuwa da wasu mutanen 186 a cikin shekarar ta 2017.

A cewar rahoton, a kalla akwai mutane miliyan 3.5 dake cikin kuncin rayuwa a kasar ta Libya, yayin da kusan mutane 400,000 suka kauracewa matsugunansu a kasar.

Matsalar rikicin siyasa, da durkushewar tattalin arziki da tashe tashen hankula na daga cikin matsalolin da suka dagula al'amurra a kasar ta Libya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China