Sin ta yi Allah wadai da harin ta'addancin da aka kai a kasar Afghanistan
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta ce, kasar Sin yi Allah wadai da harin ta'addancin da aka kai a birnin Kabul na kasar Afghanistan a jiya Alhamis. Haka kuma, kasar Sin tana goyon bayan matakan gwamnati da al'ummar Afghanistan na yaki da ta'addanci da tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku