in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya bayyana ra'ayin kasarsa dangane da batun Afghanistan
2017-09-26 19:29:55 cri
Mataimakin wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya bayyana ra'ayin kasar, dangane da batun Afghanistan, a wajen taron da kwamitin sulhun majalissar ya gudanar a jiya Litinin.

A cewar jami'in, kokarin kiyaye zaman lafiya a kasar Afghanistan, ya shafi moriyar jama'ar kasar, da burin samun ci gaba, da walwala a yankin da kasar ke ciki. Ya ce, kasar Sin ta yaba wa gwamnatin kasar Afghanistan, kan yadda take kokarin tabbatar da zaman karko, da neman samun masalaha tsakanin al'umma. Tana kuma martaba muhimmiyar rawar da kasashen dake makwabtaka da Afghanistan suke takawa, a kokarin daidaita al'amura a kasar.

A sa'i daya kuma, a cewar jami'in na kasar Sin, kasar sa na kira ga gamayyar kasa da kasa, da su goyi bayan Afghanistan, ganin yadda kasar ke fuskantar kalubaloli a fannoni daban daban.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China