in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta sanar da kawo karshen matakan soja a kasar
2017-12-19 13:58:35 cri
Jiya Litinin, rundunar sojojin tsaron kasa ta Zimbabwe ta sanar da cewa, an kawo karshen matakan soja tare da cimma burin da ake fata.

An dai kaddamar da matakan sojin ne tun daga ranar 15 ga watan Nuwamba, yayin da a yanzu haka dukkan dakarun rundunar sojoji da ta 'yan sandan kasar suka koma gudanar da ayyukansu kamar yadda suka saba.

A yayin taron manema labaran da rundunar sojojin kasar ta kira a ranar 18 ga wata, sabon kwamandan rundunar Rhilip Valerio Sibanda ya bayyana cewa, an riga an cimma burin daukar matakan soja, an gurfanar da wasu masu laifuffuka gaban kuliya, yayin da wasu suka tsere kasashen ketare.

Haka kuma, ya yi kira ga sojoji da 'yan sandan kasar da su yi hadin gwiwa wajen gudanar da ayyuka bisa dokokin kasar yadda ya kamata, domin kawar da cin hanci da karbar rashawa baki daya a duk fadin kasar, ta yadda za su ba da gudummawa ga bunkasuwar kasar ta Zimbabwe.

Daga bisani kuma, gwamnatin kasar Zimbabwe ta fidda wata sanarwa a jiya Litinin, inda ta sanar da cewa, janar Constantine Chiwenga wanda ya kaddamar da matakan soja a wannan karo ya riga ya yi ritaya, kuma an cire shi daga matsayin kwamandan rundunar sojojin kasa. Kana, za a mai da shi wani matsayi na daban a nan gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China