in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zimbabwe zai jagoranci taron jam'iyyar Zanu-PF a karon farko
2017-12-12 12:25:03 cri
Sabon shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, zai jagoranci taron musamman na jam'iyyar Zanu-PF a ranar Juma'a mai zuwa, lokacin da kuma ake sa ran jam'iyyar za ta ayyana shi a matsayin dan takarar ta a hukunce, na babban zaben kasar dake tafe a shekara mai zuwa.

Mr. Mnangagwa, wanda ya kasance shugaban kasar ta Zimbabwe na biyu a tarihin ta, ya maye gurbin tsohon shugaban kasar Robert Mugabe a watan Nuwamba, zai kuma yi takarar shugabancin kasar na shekarar 2018, kasa da shekara guda da karbe ikon kasar.

Ana sa ran wakilan jam'iyyar ta Zanu-PF kimanin 6,000 ne za su halarci taron, wanda zai gudana a birnin Harare, inda za a tabbatarwa shugaban mai ci mukamin babban sakataren jam'iyyar.

Tun a taron kwamitin tsakiyar jam'iyyar na watan Nuwamba ne dai aka tabbatarwa Mr. Mnangagwa damar takarar shugabancin kasar, karkashin jam'iyyar ta Zanu-PF mai mulkin kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China