Nijer ta sake tsawaita dokar-ta-bace domin fuskantar kalubalen ta'addanci
2017-12-16 12:30:46
cri
Gwamnatin Jamhuriyar Nijer ta fidda wata sanarwa a jiya Jumma'a dake cewa, daga ranar 18 ga watan nan da muke ciki, za a ci gaba da tsawaita dokar-ta-bace da ta sanya a yankin Diffa dake kudu maso gabashin kasar da kuma sauran yankuna shida dake yammacin kasar har tsawon watanni 3, domin fuskantar kalubalen ta'addanci. (Maryam)