in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijer ta sake tsawaita wa'adin dokar-ta-baci
2017-09-17 13:29:11 cri
Gwamnatin jamhuriyar Nijer ta sanar da tsawaita wa'adin dokar-ta-baci a jihar Diffa dake kudu maso gabashin kasar, da wasu jihohi 6 dake yammacinta, da karin watanni 3, tun daga ranar 18 ga watan nan, inda ta ce ta dauki matakin ne don tinkarar barazanar ta'addanci.

Wata sanarwa da aka fitar a shekaran jiya, ta ce kungiyar ta'addanci ta Boko Haram na ci gaba da tada zaune tsaye a jihar Diffa, yayin da 'yan ta'adda na kasashen Libya da Mali ke haifar da barazana ga tsaron yankin Sahel, wanda ya shafi mekeken filin dake yammacin kasar. Kuma wadannan batutuwa ne suka wajabta daukar matakin kara wa'adin dokar-ta-baci a wadannan wurare.

A farkon watan Yulin da ya gabata, 'yan Boko Haram sun kai hari kan wani kauye dake yankin Nguigmi na jihar Diffa, inda suka kashe mutane a kalla 9, tare da sace wasu 45. Haka zalika a karshen watan Yunin da ya gabata, 'yan Boko Haram 2 sun kai harin kunar bakin wake a wata cibiyar tallafawa 'yan gudun hijira dake yankin, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane 4, da jikkatar wasu 11.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China