Kakakin Rundunar Timothy Antigha ya ce an kama 'yan ta'addan ne yayin da suke tafiya kan dawakai 14 a kauyen Malamti dake yankin Guzamala na jihar a ranar Alhamis.
Timothy Antigha ya shaidawa manema labarai a Maiduguri babban birnin jihar cewa, sojoji biyu sun samu rauni yayin musayar wuta da ya biyo bayan kwantar baunan.
Ya kara da cewa, dakarun sun kwato alburusai da kayayyakin abinci da na ciye-ciye da dabbobi daga hannun 'yan ta'addan. (Fa'iza Mustapha)