in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Guinea: Taron dandalin SSHRF zai kara taka rawa ga ci gaban kare hakkin bil adama
2017-12-08 16:28:01 cri
Shugaban hukumar kula da harkokin kare hakkin bil adama mai zaman kanta ta kasar Guinea Mamadi Kaba ya ce, yana fatan dandalin kare hakkin bil-Adama na kasashe masu tasowa SSHRK zai iya taka muhimmiyar rawa ta fannin ci gaban harkokin hakkin bil Adam a duniya.

Jami'in wanda ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a taron dandalin da aka bude jiya a nan birnin Beijing, ya ce yana fatan kasar Sin za ta karfafa hadin kai tare da sauran kasashe a fannin kare hakkin bil adama.

Za dai a rika shirya dandalin ne a kowace shekara, ta yadda wakilan kasashe masu tasowa za su rika taruwa a Beijing don ba da shawarwari a wannan fannin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China