in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya yi kira da a mutunta muradun kasashe masu tasowa a fannin kare hakkin bil-Adam
2017-12-07 13:31:43 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi kira ga kasashen duniya da su mutunta muradun al'ummomin kasashe masu tasowa a fannin raya hakkin bil-Adam.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan cikin sakon taya murna da ya aikawa dandalin kare hakkin bil-Adam na kasashe masu tasowa da aka bude a yau a nan birnin Beijing, ya kuma mika sakonsa na fatan alheri ga dandalin, wanda ake fatan zai mayar da hankali kan yadda ake yayata batun kare hakkin bin-Adam a kasashe masu tasowa da ma duniya baki daya.

Ya ce wajibi ne, a yayata batun kare hakkin dan-Adam bisa la'akari da yanayi da bukatun al'ummomin kasashen da batun ya shafa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China