in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya bayyana damuwa game da cinikin bayi a Libya
2017-12-08 09:42:57 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya bayyana matsananciyar damuwa game da rahoton sayar da 'yan ci rani a matsayin bayi a Libya.

Kwamitin ya yi tir da wannan mummunar dabi'a wanda ya ce ta saba da hakkin dan Adam, ya na mai cewa ta na iya zama laifin take hakkin bil adama.

Kwamitin ya yi kira ga hukumomin da suka dace su gudanar da bincike kan lamarin ba tare da bata lokaci ba, domin tabbatar da kamawa da ganin wadanda ke da hannu sun fuskanci shari'a.

Kwamitin ya kuma jadadda cewa, ya damu da safarar 'yan gudun hijira da sauran mutane, ya na mai maraba da ayyukan shirin majalisar mai bada tallafi a Libya, wajen shirawa da samar da agajin jin kai ga 'yan gudun hijira da 'yan ci rani. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China