in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe wasu sojoji 4 a kasar Kamaru
2017-11-30 10:57:07 cri
Hukumomin tsaron kasar Kamaru sun tabbatar a jiya Laraba da cewa, an kai hari kan wata tashar sintiri dake yankin kudu maso yammacin kasar dab da kan iyakar kasar ta da Najeriya, lamarin da ya haddasa mutuwar wasu sojojin kasar Kamaru su 4.

Wata majiya ta hukumar tsaron kasar Kamaru ta sheda wa wakilin kwamfanin dillancin labaru na kasar Sin Xinhua cewa, mai yiwuwa ne harin na sanyin safiyar jiya, wasu ne da suka tsallaka cikin kasar ta Kamaru daga Najeriya suka kaddamar da shi. Sa'an nan ya ce an kwashe makaman sojojin da aka hallaka.

To sai akwai wadanda ke zargin cewa, mai yiwuwa 'yan a-ware da suke zaune a yankin masu magana da yaren Ingilishi ne suka kaddamar da harin.

A farkon watan da muke ciki, masu ra'ayin ballewar yankin dake magana da yaren Ingilishi daga kasar Kamaru, su hallakawa wasu 'yan sanda 4. Kafin hakan kuma, an samu barkewar zanga-zanga a yankin, inda a kalla masu zanga-zanga 10 suka rasa rayukan su, sakamakon arangama tsakaninsu da 'yan sanda.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China