Daraktan ya bayyana haka ne a yayin bikin mika tallafin kayayyaki da aka shirya a Yaounde, babban birnin kasar.
Abdoulaye Balde ya ce yayin da wasu kasashen Afirka, ciki har da Kamaru ke samun taimakon gaggawa daga kasar Sin, a waje guda kuma suna iya koyon fasahohin Sin na samu ci gaba.
A nasa bangaren, jakadan Sin dake Kamaru, Mista Wei Wenhua ya ce, batun 'yan gudun hijira da bakin haure batu ne da ya shafi shiyya-shiyya da kuma duniya baki daya.
Ya ce a matsayin ta na kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin na mayar da hankali sosai kan batun, kuma ta himmantu wajen warware matsalar. (Bilkisu)