in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani rikici ya barke tsakanin manoma da makiyaya a arewa maso gabashin Nijeriya
2017-11-23 10:16:45 cri
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta bayyana a jiya cewa, wani rikici a barke a daren ranar Litinin tsakanin makiyaya da manoma a wasu kauyuka biyu na jihar Adamawa dake arewa maso gabashin kasar Nijeriya, wanda ya haddasa mutuwar mutane 27.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Adamawa Osman Abubakar ya bayyana a jiya cewa, an yi rikici a tsakanin Fulani makiyaya da manoma dake kauyuka biyu na yankin Numan na jihar Adamawa a daren ranar 20 ga wata, rikicin da ya haddasa mutuwar mutane 27, galibin su mata da kananan yara.

Rahotanni na cewa, wasu ganau sun bayyana cewa, mutane 9 sun bace a sakamakon rikicin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China