in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi tir da harin Bam da aka kai Nijeriya
2017-11-22 11:11:20 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da harin kunar bakin wake da aka kai Nijeriya da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Cikin sanarwar da ya fitar ta hannun kakakinsa Farhan Haq, Antonio Guterres ya yi wa iyalan wadanda suka mutu da Gwamnatin da al'ummar Nijeriya ta'aziyyar rashin da suka yi, yana mai yi wa wadanda suka jikkata fatan samun lafiya, inda kuma ya yi kira da a yi gaggawar hukunta wadanda ke da hannu wajen aikata mummunan aikin.

Antonio Guterres ya kuma jadadda goyon bayan MDD ga Gwamnatin Nijeriya a yaki da take da ta'addanci da masu kaifin ra'ayin addini, ya na mai sabunta kudurin majalisar na ci gaba da mara baya ga shirye-shiryen yaki da ta'addanci.

Wani dan kunar bakin wake ne ya tada bam yayin sallar asuba a wani masallacin garin Mubin jihar Adamawa a jiya Talata, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 50. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China