in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 25 da suka samu raunuka a harin bam a masallaci a Najeriya suna cikin hayyacinsu
2017-11-23 10:10:58 cri
Wata sanarwa da babban asibitin garin Mubi ya fitar a jiya Laraba ta nuna cewa, mutane 25 daga cikin wadanda suka samu raunuka a harin kunar bakin wake da aka kaddamar a wani masallaci na garin Mubi a arewa maso gabashin Najeriya suna cikin hayyacinsu.

Ezra Sakawa, babban darakatan asibitin ya shedawa 'yan jaridu cewa, asibitin ya karbi mutane 48 wadanda harin ya shafa, 8 daga cikinsu sun mutu a yayin da ake duba lafiyarsu, kana mutane 15 an tura su zuwa asibitin gwamnatin tarayya dake Yola babban birnin jahar Adamawa.

Sakawa ya ce, ragowar mutanen dake kwance a asibitin suna cikin hayyacinsu kuma ana duba lafiyarsu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China