in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin wadanda suka mutu a harin masallaci a Najeriya ya karu zuwa 58
2017-11-23 09:16:50 cri
Hukumomi a Najeriya sunce yawan wadanda suka mutu a harin kunar bakin wake da aka kaddamar a garin Mubi dake arewa maso gabashin kasar a ranar Talata, ya karu zuwa 58.

Ezra Sakawa, babban daraktan lafiya na babban asibitin Mubi, ya shedawa manema labarai cewa, asibitin ya karbi wadanda harin ya rutsa da su kimanin 48, kuma 8 daga cikinsu sun mutu a lokacin da ake kokarin duba lafiyarsu.

Wani jami'in dan sandan yankin ya ce mutune 50 ne suka mutu a ranar Talata, ya kara da cewa, wani matashi ne wanda ba'a gano shi ba ya kaddamar da harin kunar bakin waken a cikin masallacin garin Mubin jahar Adamawa da yammacin ranar Talata.

Maharin ya tayar da bama boman ne bayan idar da salla a cikin masallacin.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, yayi Allah wadai da harin kunar bakin waken, inda ya bayyana harin a matsayin abin takaici kuma abin Allah wadai.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China