in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya bukaci a yaki masu safarar bakin haure a Afirka
2017-11-21 12:06:36 cri
A jiya Litinin ne, sakatare janar na MDD Antonio Guterres, ya bayar da sanarwa, inda ya nuna damuwa ga labarin da aka bayar cewa ana sayar da bakin haure na Afirka a kasar Libya, kana ya yi kira ga kasa da kasa dasu daura damarar yaki da irin wannan laifi.

Guterres ya karanta wannan sanarwa ga 'yan jarida cewa, bai kamata ba tsarin bauta ya cigaba da kasancewa a duniya a halin yanzu, tilastawa mutane zama bayi yana daya daga cikin miyagun ayyukan keta hakkin dan Adam, watakila zai zama laifin kiyayya ga dan Adam. Ya jaddada cewa, ya kamata a warware batun bakin haure ta hanyar jin kai, da kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa wajen yaki da sayar da mutane.

Guterres ya kalubalanci hukumar da abin ya shafa da ta yi bincike kan batun ba tare da bata lokaci ba, kuma ta gurfanar da masu aikata laifin a gaban kotu. Ya bayyana cewa, ya riga ya bukaci hukumomin MDD su yi bincike kan batun.

Kafofin watsa labaru na kasar Amurka sun bayar da labari a makon da ya gabata cewa, an sayar da bakin haure na Afirka da suka tsaya a wurare daban daban na kasar Libya a matsayin bayi. A ranar 19 ga wannan wata, gwamnatin hadin gwiwar al'ummar kasar Libya ta sanar da yin bincike kan batun. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China