in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi na'am da sakamakon taron COP karo 23
2017-11-19 12:24:32 cri
A yayin da aka karkare taron masu ruwa da tsaki na kasa da kasa a fannin sauyin yanayi karo na 23 wato COP 23 a ranar Asabar, wakilin musamman na kasar Sin kan al'amuran sauyin yanayi Xie Zhenhua, ya bayyana cewa, duk da kasancewar taron tattaunawar da aka gudanar game da sauyin yanayin bai gamsar 100 bisa 100 ba, amma an samu nasara wajen cimma matsaya guda daga dukkan bangarorin da abin ya shafa, kana ya bukaci manyan kasashen duniya mafiya karfin ci gaba da su sauke nauyin dake bisa wuyansu.

Xie, ya bayyana cewa, daftarin bayanan da aka cimma matsaya kansu sun tabo dukkan muhimman batutuwa dake kunshe cikin yarjejeniyar da aka kulla a birnin Paris game da sauyin yanayi.

Taron na COP 23 ya fayyace tsarin da ya kamata a bi wajen shirya taron tattaunawar shekarar 2018, kana ya amince da a hanzarta aiwatar da yarjejeniyar sauyin yanayin gabanin shekarar 2020, da kuma daukar matakan takaita fitar da hayaki mai gurbata yanayi.

Wakilin na Sin ya ce, sauye sauye da kuma fitar da managartan tsare tsaren da kasashen da suka halarci taron suka yi ya aza wani harsashe wanda zai tabbatar da cimma nasarar aiwatar da yarjejeniyar sauyin yanayi ta birnin Paris kamar yadda aka tsara tun da farko. Ya kara da cewa suna fata dukkan bangarorin da abin ya shafa za su mutunta tsarin daidaito, kuma za su amince da sauke nauyin dake wuyansu, kana su bi dukkan sharrudan dake wuyan kowace kasa don tabbatar da ganin an cimma nasarar aiwatar da yarjejeniyar sauyin yanayi ta birnin Paris yadda ya kamata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China