in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin ta ce gaskiya da adalci ne manyan ginshikan COP22
2016-11-08 09:53:34 cri
Wani kusa a gwamnatin kasar Sin ya fada cewa, yin gaskiya da adalci su ne manyan ginshikan taron masu ruwa da tsaki karo na 22 wato (COP22).

Xie Ji, mataimakin babban wakilin kasar Sin a taron karawa juna sani na COP22 da ake gudanarwa a birnin Marrakech na kasar Morocco, ya bayyana cewar, akwai bukatar dukkanin bangarorin da abin ya shafa su cimma matsaya game da aiwatar da yarjejeniyar Paris.

A taron MDD kan sauyin yanayi a karon farko da aka gudanar tun bayan amincewa da yarjejeniyar Paris, wanda aka gudanar kwanaki 3 da suka gabata, an bude taron na COP22 ne da safiyar ranar Litinin, mahalarta kusan dubu 20 ne daga sassan duniya da dama, wadanda ake sa ran za su tattauna na tsawon kwanaki 11, game da batutuwan da suka shafi yadda za'a aiwatar da yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris cikin nasara. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China