in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kira da a mutunta yarjejeniyar Paris yayin bude taron sauyin yanayi na MDD a Bonn
2017-11-07 10:00:07 cri

An bude taro na 23, na kasashen da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar sauyin yanayi jiya Litinin a birnin Bonn na kasar Jamus, inda aka yi kira da a mutunta yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris.

Taron na da nauyin samar da hanyoyin aiwatar da yarjejeniyar wadda kusan dukkan kasashen duniya suka amince da ita a shekarar 2015.

Yarjejeniyar ta Paris na da nufin magance matsalolin sauyin yanayi ta hanyar rage fitar da gurbatacciyar iska tare da sanya matsakaicin mataki na ganin yanayin zafin duniya bai dara yanayin da yake kafin zuwa masana'antu da maki biyu na ma'aunin Celsius ba.

Yayin bude taron, Sakatariyar zartarwa ta hukumar kula da sauyin yanayi ta MDD Patricia Espinosa ta ce, "idan aka hada yarjejeniyar da muradun ci gaba masu dorewa, to akwai tartibiyar hanya ta magance sauyin yanayi da samar da dawwamammen ci gaba."

Da take zayyana ayyukan da gwamnatocin kasashe za su shawo kansu yayin taron na Bonn, ta ce manufar ita ce, daukar managartan matakan tabbatar da kammala tsare-tsare ayyukan yarjejeniyar a kan lokaci, tare kuma da karfafa hanyoyin aiwatar da ita.

Yayin wani taron manema labarai gabanin bude taron, wakilin musammam na kasar Sin kan batun sauyin yanayi Xie Zhenhua ya ce kasarsa na fatan maharlarta taron za su samar da hanyoyin dake bayyana abubuwan da ake bukata daga dukkan bangarorin dake cikin yarjejeniyar ta Paris. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China