Wata sanarwa da Kakakinsa Garba Shehu ya fitar, ta bayyana girgizar kasa da aka yi a yammacin lardin Kermanshah na Iran a matsayin mai ciwo matuka.
Sanarwar ta kuma bayyana iftila'in da asarar da ya haifar a matsayin abun bakin ciki mai tada hankali.
Shugaba Muhammadu Buhari ya kuma mika irin wannan jaje ga Gwamnati da al'ummar Iraqi bisa asarar dukiya da rayuka da suka yi sanadiyyar girgizar kasar da ta auku akan iyakar kasar da Iran. (Fa'iza Mustapha)