in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos ya baiwa 'yan sanda gudummawar kayayyakin aiki
2017-11-10 13:12:28 cri

A jiya ne karamin ofishin jakadancin kasar Sin dake Lagos a tarayyar Najeriya, ya baiwa 'yan sanda gudummawar baburan sintiri guda 9 da na'urorin sanya daki, a wani mataki na inganta ayyukansu.

Da yake mika kayayyakin, babban jami'i mai kula da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos Chao Xiaoliang, ya bayyana kudurin kasar Sin na ci gaba da taimakawa shirye-shiryen jami'an tsaro na kare rayuka da dukiyoyin jama'a, kamar yadda suka nuna a wannan lokaci.

Da yake karbar kayayyakin, mataimakin sifeto janar na 'yan sanda mai kula da yankin Lagos Ibrahim Adamu ya ba da tabbacin cewa, za a yi amfani da kayayyakin yadda ya kamata.

Bikin mika kayayyakin ya kuma samu halartar manyan jami'an 'yan sandan Najeriya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China