in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Inganta hadin-gwiwa tsakanin Sin da Jamus da Afirka zai taimaka ga samar da makamashin da ake iya sabuntawa a Afirka
2017-11-16 13:42:58 cri
Jiya ne, wakilai daga kasashen Sin, Jamus, gami da na kasashen Afirka, wadanda suka halarci wani babban taro kan batun sauyin yanayi a birnin Bonn na kasar Jamus suka yi wani taron karawa juna sani, inda suka bayyana cewa, bullo da wani tsarin hadin-gwiwa tsakanin kasashen Sin, Jamus da kasashen Afirka, zai taimaka sosai wajen cimma burin matsalar tinkarar sauyin yanayi a fadin duniya, da neman samun ci gaba mai dorewa.

Jiya Laraba ta kasance ranar Afirka a yayin babban taron sauyin yanayi dake gudana a birnin Bonn. Cibiyar nazarin harkokin ci gaba ta kasar Jamus gami da cibiyar bada shawarwari kan harkokin Sin da Afirka mai hedikwata a birnin Kӧln na Jamus, sun shirya wannan taron karawa juna sani, inda wakilan gwamnatocin Sin da Jamus da Afirka, gami da na wasu cibiyoyi da kungiyoyin kasa da kasa suka tattaunawa kan yadda za su fadada hadin-gwiwa a fannin tinkarar matsalar sauyin yanayi da neman ci gaba mai dorewa.

Kasar Jamus ta dade tana taimakawa kasar Sin tinkarar matsalar sauyin yanayi, kana, tana samar da dimbin taimako ga kasashen Afirka a fannin raya makamashin da ake iya sabuntawa. Ita kuma kasar Sin, ta jima tana kokarin raya amfani da makamashin da ake iya sabuntawa a nahiyar Afirka. Saboda haka, inganta hadin-gwiwa tsakanin wadannan bangarori uku, wato Sin da Jamus da Afirka, zai kara kokarin da ake na bunkasa makamashin da ake iya sabuntawa a kasashen Afirka, da neman ci gaba a wasu sauran fannoni da dama. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China