in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya gana da shugaban tawagar kasar Sin da ke halartar taron sauyin yanayi a kasar Jamus
2017-11-16 13:35:11 cri
Jiya Laraba ne, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya gana da shugaban tawagar kasar Sin a taron MDD kan batun sauyin yanayi na birnin Bonn na kasar Jamus, kana wakili na musamman na gwamnatin Sin kan harkokin sauyin yanayi, Mista Xie Zhenhua, inda bangarorin biyu suka yi musanyar ra'ayi dangane da batutuwa da dama, ciki har da karfafa hadin-gwiwa tsakanin Sin da MDD a fanin tinkarar sauyin yanayi, da kara kokarin shawo kan wannan matsala tsakanin kasashen duniya.

Guterres ya ce, a 'yan shekarun nan, kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a fannonin da suka shafi raya tattalin arziki, muhalli da yanayi, wadda ta kasance babbar aminiyar MDD. A bana, shugaban kasar Sin ya gabatar da jawabi a gun taron dandalin tattaunawa na Davos gami da hedikwatar MDD dake birnin Geneva, inda ya jaddada cewa, kasar Sin za ta martaba yarjejeiyar Paris, kana, rahoton da aka fitar a wajen babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 ya ce, kasar Sin za ta yi iyakacin kokarinta wajen neman ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, al'amarin da ya samu yabo matuka daga MDD.

A nasa bangaren, Xie Zhenhua ya ce, yana fatan MDD za ta kara fadakar da kasashe daban-daban kan alakar kut da kut dake tsakanin tinkarar sauyin yanayi da burin neman ci gaba mai dorewa nan da shekara ta 2030, a wani mataki na raya harkokin duniya ba tare da gurbata muhalli ba kuma cikin dogon lokaci. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China